Connect with us

Labarai

Sarki Sanusi ya shawarci gwamantin Kano kan ta tabbatar ana hukunta masu kashe mutane

Published

on

‎Mai martaba sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu ya shawarci gwamnatin jihar Kano kan ta yi duk mai yiyuwa wajen ganin an zartar da hukunci kisa a kan duk wani mutum da aka tabbatar ya na da hannu wajen kisan mutanen da basu ji ba basu gani ba.

‎‎Khalifa Muhammadu Sunus  ya yi wannan kira ne lokacin da yake zantawa da manema labarai kan kisan wata mata da yayanta a unguwar Dorayi Chiranci da ke yankin karamar hukumar Kumbotso.

A wani labarin kuma Mai martaba sarkin Kanon ya yi kira ga hukumar Zakka da hubusi ta jihar da ta dage wajen karbo Zakka a hannu mawadata da manoma don taimaka wa marasa karfi.

‎Sarkin ya bayyana haka ne lokacin da shugaban hukumar zakka da hubusi ta jihar Kano karkashin jagorancin shugabanta  Barista Habibu Dan Almajiri Fagge Suka ziyarce shi a fadarsa.

‎Barista Habibu Dan Almajiri Fagge yace sun zo fada ne don gabatar da kansu da kuma neman alfarmar Mai martaba sarkin daya yi kira ga mawadata kan su rinka taimakawa marasa karfi duba da yanda watan azumi yake gabatowa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!