Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Muna goyon bayan ilimi kyauta kuma wajibi -sabon Sarkin Kano

Published

on

Sabon sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya jaddada goyon bayan sa ga shirin ilimi kyauta kuma wajibi na gwamnatin jihar Kano.

Mai martaba Aminu Ado Bayero, yace zasu yi duk mai yiwuwa karkashin ikon su don ganin shirin ya tabbata da amfanar da al’umma, san nan ya yi  kira ga dukkanin Al’umma dasu mayar da hankali wajen taimakawa makarantu a wani mataki na bunkasa harkokin ilimi a fadin jihar nan.

Sabon sarkin, ya bayyana hakan ne a yayin ziyarar da ya kai makarantan firamare ta gidan makama don duba halin da karatun makarantar yake gudana.

Sabon Sarkin Kano yaje gidan mahaifiyar sa don neman tabarraki

Ana tsaka da nada sabon sarkin Bichi

Mai martaba Aminu Ado Bayero,  ya ce wajibi masu hannu da shuni da  su shigo cikin  harkokin sha’anin ilimi domin kuwa gwamnati kadai baza ta iya ba.

A nasa jawabin shugaban hukumar kula da makarantun sakandire na jihar kano, Dr Bello Shehu,  ya nemi hadin kan  masarautun gargajiya don ganin  shirin ya cimma nasara.

Shamsu Dau Abdullahi, wakilin mu da ya halarci wajen taron  ya ruwaito cewar yayin ziyarar sabon sarkin  ya samu rakiyar manyan hakiman sa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!