Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sarkin Hausawan Afrika ya nemi dalibai su koyo sarrafa harshen Hausa

Published

on

Sarkin Hausawan Afrika kuma Sardaunan Jihar Agadaz Dakta Abdulkadir Labaran Koguna, ya bukaci dalibai da su mayar da hankali wajen koyo tare da sarrafa harshen hausa.

Dakta Abdulkadir Labaran na bayyana hakan a yau ta cikin shirin “Barka da Hantsi” na nan tashar freedom Rediyo, wanda ya mayar da hankali kan ranar Hausa ta duniya da za a gudanar a gobe Laraba.

Dakta Labaran ya kuma ce, harshen hausa na taka rawa wajen dabbaka al’adun bahaushe, yana mai cewa, matasan yanzu na kokarin aron al’adun wasu harsunan wanda bai daidai ba ne.

A cewar sa, harshen hausa ya mamaye kasashe hamsin da tara a fadin duniya, wanda ya ba su damar yin sarautu a wasu kasashen a bangaren harshen na hausa.

Shi ma da ya kasance cikin shirin, sarkin kungiyar daliban Hausa ta kasa Malam Nura Sulaiman Janburji, ya ce harshen hausa na da alfarma ta yadda a kasashen ketare akan bai wa dalibai damar kafa daula.

Bakin biyu, sun yi kira ga gwamnatoci a dukkanin matakai da su dabbaka harshen hausa a majalisun kasar nan don kare marbatar sa a idon duniya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!