Labarai
Sarkin Kano ya buƙaci gwamnati da masu hali su taimaki talakawa
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2023/04/Emir-Aminu-Ado-Bayero.png)
Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yi kira ga gwamnatoci da mawadata da su tallafa wa marasa ƙarfi domin sauƙaƙa musu matsin rayuwa da a ke fama da shi.
Sarkin ya buƙaci hakan ne wata ganawa da ya yi da manema labarai a fadarsa a wani ɓangare na bikin ranar agaji ta duniya.
Ya ce, “A matsayinmu na shugabani kuma waɗanda ke tare da talakawa kuma muke sauraron koke-kokensu a kullum, ya zama wajibi mu ƙara jan hankalin wadanda ke da wadata su riƙa tallafa wa makobtansu waɗanda ba su da hali”.
A gefe guda kuwa sarkin ya yi bayanin cewa koda a kwanankin baya ya bayyanawa shugaban kasa halin da al’umma ke ciki na matsin rayuwa a wani zama da shugaban ya yi da sarakuna.
Rahoton: Shamsu Da’u Abdullahi
You must be logged in to post a comment Login