Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Saudiyya:Ta ɗauki nauyin aiki ga jariran da aka haifa a manne

Published

on

Gwamna Abba Kabir ya yi bankwana da wasu tagwayen da suke manne da juna domin yi musu aikin a ƙasar Saudiyya

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yabawa masarautar Saudiyya karkashin jagorancin Sarki Salman Bin Abdul’aziz kan daukar nauyin yi wa jarirai tagwaye a Kano tiyata a wani asibiti da ke kasar Saudiyya a birnin Riyadh

Wannan na ƙunshe ne ta cikin wata takarda da ɗauke da sa hannun sakataren yaɗa labaran Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya kuma rabawa manema labarai

Da yake jawabi a lokacin da yake bankwana da iyayen tagwayen jarirai a filin jirgin sama na Aminu Kano, gwamnan ya bayyana irin alherin da Sarki Salman ya yi a matsayin wani aiki da Allah ya saka masa da ya dace a yi koyi da shi

Gwamna Yusuf wanda ya yi addu’ar Allah ya dore da dankon zumuncin da ke tsakanin Kano da Masarautar Saudiyya, ya bayyana cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba a kokarinta na dawo da martabar da aka rasa a bangaren kiwon lafiya a jihar

Gwamnan ya kuma ce ba da daɗewa ba Likitocin Saudiyya sunzo Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, domin kula da marasa lafiya da ke fama da ciwon zuciya da matsalar idanu kyauta

Don haka ya yi addu’a ga jariran tagwayen da suke hade da juna don samun nasarar aikin tiyatar da aka yi musu sannan kuma suka dawo da rai a matsayin mutane biyu masu zaman kansu

Da yake jawabi tun da farko, karamin jakadan Saudiyya a Kano, Sheikh Khalil Al’adamawi ya bayyana cewa, irin wannan shiri na nuni ne da yadda Saudiyyar ta himmatu wajen gudanar da ayyukan jin kai da kuma sadaukar da kai wajen taimakon mabuƙata

Ya kuma kara da cewa, ana mika wannan karamcin ne ga mabukata ba tare da la’akari da kasarsu ko asalinsu ba, yana mai jaddada cewa masarautar Saudiyya ce kan gaba wajen samar da kayayyakin jin kai na kasa da kasa

Daga nan ne karamin jakadan ya bayyana cewa za a kwantar da iyayen tagwayen da suka hade a birnin Riyadh, kuma za a ba su tsarin tallafi don samun kwanciyar hankali da taimako a tsawon tafiyar su

A nasa jawabin, mahaifin tagwayen da suka a haɗe, Malam Hassan Isa Kano ya bayyana matukar godiyar sa ga mai kula da masallatai biyu masu tsarki, Salman Bin Abdulaziz bisa daukar nauyin yi wa tagwayen, Hassana da Husaina aikin tiyata, yana mai addu’ar Allah ya jikansa ya saka masa da iyalansa da jannatul Firdausi

Ya kuma yabawa gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa kauna da kulawar da ya nuna musu tare da ba su lokaci domin yi musu bankwana a filin jirgin sama a yau

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!