Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sauya sheƙa: Kotu ta sauke gwamnan jihar Ebonyi da mataimakinsa

Published

on

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci gwamnan jihar Ebonyi Dave Umahi da mataimakinsa Eric Kelechi Igwe da su gaggauta ficewa daga ofishinsu bayan sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC ba bisa ƙa’ida ba.

Mai shari’a Inyang Ekwo, a wani hukunci da ya yanke a ranar Talata, ya bayyana cewa bayan ficewa daga jam’iyyar da suka lashe zaɓen.

Mai shari’a Ekwo ya umurci hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ta karɓi sunayen mambobinta daga hannun jam’iyyar PDP domin maye gurbin Umahi da Igwe, domin cike ragowar wa’adin mulkinsu, ko kuma ta sake gudanar da sabon zaɓe domin maye gurbin nasu.

Alƙalin kotun ya kuma haramtawa Umahi da Igwe ci gaba da bayyana kan su a matsayin gwamna da ataimakin gwamnan Jihar Ebonyi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!