Connect with us

Labarai

SERAP ta bukaci shugaban NNPCL ya binciko wadanda suka karkatar da kudaden Mai

Published

on

Shirin tabbatar da ganin gwamnati na bin ka’idoji wajen gudanar da ayyukanta SERAP ta bukaci babban jami’in gudanarwa na Kamfanin Mai na Ƙasa  Bayo Ojulari da ya gano wadanda ke da hannu wajen karkatar da kudaden man da ake zargi sun bace kimanin  Sama da Naira Biiyan 22 tare da mikawa Hukumar EFCC da ICPC domin gurfanar da su a gaban kotu. 

SERAP ta kuma nemi a dawo da dukkan kudaden da suka ɓace cikin baitulmalin ƙasa ba tare da wani jinkiri ba, tana mai cewa kamata ya yi gwamnati ta dauki matakin gaggawa wajen kare dukiyar jama’a da hana irin wannan al’amari sake faruwa.

SERAP ta bayyana haka ne a cikin wata wasika mai kwanan wata 25 ga Oktoba, 2025, wacce mataimakin darakta na kungiyar, Kolawole Oluwadare, ya sanya wa hannu. 

Rahoton na zargin bacewar kudaden ya fito ne daga rahoton shekara ta 2022 da Auditor-General na Ƙasa ya wallafa a ranar 9 ga Satumba, 2025.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!