Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari ya bukaci manyan hafsoshin tsaro su kara jajircewa akan aikin su

Published

on

Shugaban kasa muhammadu Buhari ya bukaci manyan hafsoshin tsaron Najeriya da su kara jajircewa wajen tabbatar da cikakken tsaron rayuka da dokiyoyin al’umma.

Muhammadu Buhari na wadannan kalaman ne lokacin da yake ganawa da manyan hafsojin tsaron  a fadar Asorok da ke birnin tarayya Abuja.

Shugaban kasar ya kuma bukaci sufeto janar na ‘yan sandan kasar nan da su yi kokari wajen dakile ayyukan ‘yan’ta’adda da masu garkuwa da mutane suna garkuwa da su.

Daga cikin wadanda suka halarci taron sun hada da: Minstan tsaro Burgediya janar Mansur Dan Ali mai ritaya da babban hafsan tsaro Janar Abayomi Olonishekin , da babban hafsan sojin kasa Laftanal Janar Tukur Yusuf Buratai, da kuma babban hafsan sojin ruwa Vice Admiral Ibok-Ete.

Sauran sun hada da: shugaban sashen bangaren tsare tsare na rundunar soji ta kasa Air Vice Marshal Emmanuel Achebi sai kuma mai rikon mukamin sufeto janar na ‘yan ’sandan kasar nan Muhammad Adamu.

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala ganawa da Shugaban kasa, Babban hafsan Sojin ruwa Vice Admiral Ibok-Ete, ya ce, ana samun raguwar adadin masu garkuwa da mutane a kasar nan, sai dai ya ce, yayin tattaunawar wasu daga cikin hafsoshin sun yiwa shugaban kasa bayani kan wasu sabbin hanyoyin da za’abi wajen kawo karshen matsalar yan’tadda a fadin kasar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!