Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari zai shirya liyafar cin abinci ga wasu Shugabannin duniya

Published

on

Yanzu haka dai ana gudanar da faretin girmamawa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da mataimakin sa Farfesa Yemi Osinbajo a dandalin Eagles square da ke birnin tarayya Abuja, a wani bangare na gudanar da taron bikin ranar dimokradiyya.

Rahotanni sun bayyana cewa daga cikin wadanda suka halarci taron akwai sabon shugaban majalisar dattawa Sanata Ahmed Lawan da takwaran sa na wakilai Femi Gbaja-bia-mila sai kuma wasu daga cikin manyan shugabanni.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya fara zagaye sojojin da suke je fareti a matsayin mafarin bude taro, wanda ke gudana yanzu haka a filin wasa na Eagles square.

Daga cikin shugabannin da suka halarci taron akwai na kasashen Rwanda, Sierra Leone, Ghana, Namibia, Niger, Congo, Liberia, Gambia da kuma Guinea Bisau.

Sauran sun hadar da mataimakan shugabannin kasashen Sudan, Uganda ta kudu da na Zimbabwe, da kuma Masar, sai wakilan Jamhuriyar Benin, Equatorial Guinea, Gabon, Jamhuriyar Cek, Faransa, Ireland, Japan, Mali, Kenya, Morroco, Malawi da kuma Belgium.

A cewar rahotanni mukaddashin babban jojin Najeriya da shugabar ma’aikata ta tarayya da kuma babban sufeton ‘yan sandan kasar nan hadi da sauran shugabannin hukumomin tsaro ne suka halarci taron.

Sauran sun hadar da jagoran jam’iyyar APC na kasa Sanata Bola Ahmed Tinubu da gwamnonin Kano da Kogi, Yobe, Kwara, Kebbi, Ekiti, Kaduna da kuma Anambra.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!