Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Tinubu ya ayyana 7 ga Afrilu a matsayin ranar Ƴan sanda

Published

on

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana ranar 7 ga watan Afrilu a matsayin ranar ‘yan sanda ta ƙasa.

Shugaba Tinubu, wanda mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya wakilta, ya bayyana hakan a daren ranar jiya Litinin yayin bikin karramawar da ‘yan sanda suka yi a otal ɗin Transcorp Hilton da ke birnin tarayya Abuja.

Ya bayyana sake fasalin tunanin hukumomi da kuma tunawa da jami’an ‘yan sanda a matsayin wani muhimmin abu a yunkurin gwamnatinsa na mayar da rundunar zuwa cibiya ta zamani, kwararru da kuma rikon amana.

Ya ce gwamnatinsa ta bullo da sauye-sauye masu yawa domin farfado da rundunar ‘yan sandan kasar tun bayan hawansa ofishi a shekarar 2023.

Don haka ya jadadda bukatar shigar da maza da mata na rundunar wajen horas da su da kuma samar musu da kwararrun da ake bukata domin gudanar da aiki mai wahala na aikin ‘yan sanda na zamani.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!