Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya buƙaci gwamnoni su fifita walwalar mutanen da suke jagoranta

Published

on

Shugaban kasa Bola Tinubu ya buƙaci gwamnoni da su fifita walwalar mutanan da suke shugabanta musamman na yankunan Karkara, ta hanyar bunƙasa wutar lantarki da ayyukan noma domin kawar da talauci.

 

Kiran na zuwa ne bayan gabatar da wani shirin gwamnati na musamman kan bunƙasa tattalin arziki a matakin mazaɓu da aka yi wa laƙabi da ‘Renewed Hope Ward Development Programme wanda ministan kasafi da tsare-tsare ya gabatar a taron majalisar tattalin arzikin ƙasa.

 

Manufar sabon shirin shi ne tabbatar da bunƙasar tattalin arziki ta hanyar taimaka wa mazaɓun ƙasar nan dubu 8,809 a faɗin jihohi 36, kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasar ta bayyana.

 

Shugaba Tinubu ya kuma buƙaci gwamnonin ƙasar nan da su yi duk mai yiwuwa wajen tallafa wa rayukan ƴan ƙasar daga tushe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!