Labarai
Shugaba Tinubu ya kafa asusun tallafi ga sojojin da suka jikkata da wanda suka rasu a bakin aiki

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya kafa sabon asusun tallafi na musamman domin taimaka wa sojojin Najeriya musamman waɗanda suka jikkata a bakin aiki da kuma iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.
Shugaban ya bayyana haka ne a ranar Lahadi, yayin bikin cikar sa shekaru 74, inda ya ce hakan wata hanya ce ta girmama sadaukarwa da jarumtar jami’an soji.
Ya kuma umarci Akanta Janar na Tarayya da ya buɗe asusu na musamman domin gudanar da wannan shiri,
Shugaba Tinubu ya yi alƙawarin bayar da duk albashinsa tun daga lokacin da ya hau mulki a matsayin tushen fara wannan asusu.
Ya kuma yi kira ga gwamnoni, ‘yan majalisar dokoki, kamfanoni masu zaman kansu da sauran masu hannu da shuni da su mara wa shirin baya.
You must be logged in to post a comment Login