Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya sake aika wa majalisar dokokin buƙatar ƙara ciyo bashin Dala miliyan 347

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake miƙa wa majalisar dokoki  buƙatar ƙara ciyo bashi na Dala miliyan 347 daga ƙetare, ƙarƙashin shirin ciyo bashi na gwamnatin tarayyar na shekarun 2025 zuwa 2026.

 

Buƙatar na zuwa ne cikin wata takarda da Tinubu ya aikewa majalisar, wadda shugaban majalisar wakilai Tajudeen Abbas ya karanto a zamansu na jiya Laraba.

 

Tinubu ya ce ciyo bashin ya zama dole saboda buƙatar ƙarin kuɗi da aka yi a aikin babbar hanyar Lagos zuwa Calabar, wanda ya tashi daga Dala miliyan 700 zuwa Dala miliyan 747, ƙarin Dala miliyan 47.

 

Ko a ranar Talatar makon nan sai da majalisar datttawa ta amincewa shugaba Tinubu ciyo bashin Dala biliyan 21 daga ƙetare.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!