Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro tare da naɗa wasu

Published

on

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya ya sauke babban hafsan Soja Janar Christopher Musa da sauran hafsoshin tsaron a wani sauyi a tsarin jagorancin sojin Najeriya domin ingantawa tare da da ƙarfafa sha’anin tsaro.

Ta cikin wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa ta fitar mai ɗauke da sa hannun ɗaya daga cikin masu taimaka wa shugaban a harkar yaɗa labarai, Sunday Dare, Tinubu ya yi musu fatan alkairi tare da bayyana sunayen sabbin hafsoshin da za su maye gurbin waɗanda aka sauke ɗin.

BBC ta ruwaito cewa, Sababbin hafsoshin da shugaban ya naɗa sun haɗa da:

1. Janar Olufemi Oluyede – Hafsan hafsoshi

2. Manjo Janar W Sha’aibu – Hafsan sojojin ƙasa

3. Air Vice Marshall S.K Aneke – Hafsan sojin Sama.

4. Rear Admiral I. Abbas – Hafsan sojin ruwa

5. Manjo Janar E.A.P Undiendeye – Shugaba sashen tattara bayan sirri na soji.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!