Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan gillar da aka yi a unguwar Dorayi

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tunibu yayi kakkasur suka kan kisan gillar da aka yiwa wata matar aure mai suna Fatima Abubakar da yayanta shida a unguwar Dorayi Chiranci a jihar Kano.

 

Cikin wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar tace shugaba Tinubu ya bayyana lamarin a matsayin munmunan rashin imani da tausayi wanda ya girgiza al’ummar dama kasa baki daya.

 

Tunubu ya nuna matukar alhini kan wannan munmunan iftila’in tare da mika ta’aziyya ga iyalan mamatan.

 

Shugaban ya kuma yaba wa rundunar yan sanda bisa gaggawar daukar mataki na kama wadanda ake zargi da aikata laifin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!