Labarai
Shugaba Tinubu ya zaɓi sabon shugaban hukumar Alhazai ta kasa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya zaɓi Amb. Ismail Abba Yusuf a matsayin sabon shugaban hukumar alhazai ta ƙasa (NAHCON).
Wata sanarwa da ta fito daga mai bai wa shugaban shawara kan yaɗa labarai da dabaru Bayo Onanuga, ta ce a yau Laraba ne shugaba Tinubu ya aike da wasika zuwa ga shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, inda ya bukaci a gaggauta tabbatar da Ambasada Yusuf ya maye gurbin Farfesa Abdullahi Usman, wanda ya yi murabus a farkon wannan makon, bayan shafe kimanin watanni 14 yana kan muƙamin.
You must be logged in to post a comment Login