Connect with us

Labarai

Tinubu, ya umarci dakarun rundunar sojin ƙasar nan da su canja salon yaki da ‘yanta’adda a Katsina

Published

on

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya umarci dakarun rundunar sojin ƙasar nan da su canja salon da suke bi wajen fatattakar ƴan bingida a jihar Katsina ta hanyar yin amfani da na’urori na zamani wajen sanya ido kan matsalar tsaro.

Shugaba Tinubu, bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gwamnan jihar ta Katsina Dikko Radda da wasu shugabannin jihar a fadar mulki ta Villa da ke Abuja.

Tinubu ya kuma jaddada muhimancin magance matsalar tsaro a faɗin ƙasar nan, ya na mai cewa, gwamnatinsa za ta ƙara ɗaukar matakan tsaro na cikin gida, ciki har da yiwuwar kafa ƴan sandan jihohi da ƙarfafa masu gadin dazuka.

Haka kuma, ya buƙaci a rika samun rahoton aikin jami’an tsaro kullum daga Katsina.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya kuma bayyana cewa, ya zama dole gwamnatinsa ta kare rayukan jama’a da kuma wuraren ibada da kasuwanci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!