Connect with us

Labarai

Sojoji sun daƙile harin ‘yan Boko Haram

Published

on

Dakarun sojin Najeriya sun daƙile wani hari da ‘yan tada kayar baya na Boko Haram suka kai wani sansanin soji da ke Buni Yadi, a ƙaramar hukumar Gujba ta Jihar Yobe.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an dakarun sun hallaka ‘yan ta’addan da dama, sai dai an samu asarar rayukan  wasu daga cikin jami’an  sojin.

Wasu mazauna yankin sun shaida wa manema labarai cewa, sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa  a lokacin da suka  samu  ƙarin runduna, inda hakan ya tilasta wa ‘yan ta’addan tserewa.

Wani soja ya tabbatar da cewa sun kashe ‘yan ta’adda da dama tare da ƙwato motoci biyu da makamai da dama daga hannun su.

Sai dai wani daga cikin mazauna ƙauyen, wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce, an samu zaman lafiya bayan faruwar harin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!