Labarai
Sojoji sun kashe ƴanbindiga 45 a jihar Katsina

Sojojin ƙasar nan sun kashe ƴanbindiga 45 da suka kai hari wani ƙauye a jihar Katsina da ke arewacin ƙasar.
Lamarin ya faru ne ranar Juma’a da maraice kamar yadda hukumomin jihar suka tabbatar.
Rahotonni sun ce tun da farko ƴanbindigar waɗanda suka taso daga jihar Zamfara mai makwabtaka, sun kai hari ƙauyen Alhazawa na ƙaramar hukumar Danmusa a ranar Alhamis domin satar shanu.
To sai dai mazauna garin sun nuna turjiya inda suka kashe huɗu daga cikin maharan.
Kwana guda bayan hakan ne kuma ƴanbindiga suka sake taruwa da nufin ɗaukar fansa kan mazauna ƙauyen, inda suka ci karo da sojoji a kan hanyar tasu, lamarin da ya haifar da musayar wuta tsakani.
You must be logged in to post a comment Login