Connect with us

Labarai

SUBEB ta yaba da yadda Musa baƙar Kano ke gudana

Published

on

Hukumar kula da ilimin bai-daya ta jihar Kano SUBEB, ta nuna gamsuwarta kan yadda  musabakar karatun Al-Qur’ani Mai tsarki ke gudana a kwanakin nan.

Shugaban hukumar Alhaji Yusuf Kabir, da ya samu wakilcin babban jami’i a hukumar Malam Magaji Yusuf, ne  bayyana hakan a Litinin ɗin makon na yayin da aka shiga rana ta biyar da fara musabakar.

Ya kuma yaba da kokarin kwamitin amintattu na  musabakar Al-Qur’anin na jihar Kano bisa yadda suke gudanar da ayyukansu.

Da ya ke ganawa da manema labarai, Alhaji Sabiu Bako mamba a kwamitin  shirya musabakar ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta ƙarasa samar da kyautukan da za a raba wa zakarun da za su samu nasara a  musabakar, kafin ranar da za a kammala.

Yanzu haka dai, an shiga ɓangare na izu sittin tare da Tajawidi a fannin maza.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!