Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Musabakar alkur’ani na kara zaburar da dalibai – Shiekh Umar Fagge

Published

on

Fitaccen malamain addinin musulunci anan Kano Sheikh Umar Sani Fagge ya bayyana musabakar alkurani mai girma a matsayin abinda ke nesanta al’umma daga duhun jahilci da kuma kara habbaka addinin musulunci.

Sheikh Umar Sani Fagge ya bayyana hakan ne a yau yayin da yake gabatar da mukala a taron musabakar alkurani ta kasa da aka gudanar a jami’ar Bayero da ke nan Kano.

Sheikh Fagge ya ce, musabakar alqurani na taimakawa wajen kara zaburar da dalibai da kuma sanya soyayyar karatun alkur’ani a zakatan daliban.

Da yake jawabi gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnati na shirin bude dakin karatu na musamman ga daliban islamiyya, tare da sanya na’urorin da za su saukakawa dalibai bincike.

Musabakar itace karo na 35 wanda kuma gwamnatin Kano ce ta dauki nauyin gudanar da ita.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!