Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Super Eagles za ta fafata da Côte d’Ivoire da Tunisia

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagles za ta kara da kasar Côte d’Ivoire da kuma Tunisia a wasannin sada zumunta na kasa-da-kasa a watan Oktoba mai zuwa.

Najeriya dai za ta fafata da kasar Côte d’Ivoire a ranar 9 ga watan na Oktoba, kafin daga baya su hadu da kasar Tunisia bayan kwanaki 4.

Shugaban hukumar NFF, Amaju Pinnick, ya ce, za’a gudanar da wasannin guda biyu ne a kasar Austria.

Shugaban, ya ce, “Hukumar ta ci gaba da tattaunawa wajen ganin an samu damar wasannin sada zumunta, tsakanin Najeriya da wasu kasashen, sai kuma gashi an samu damar yin wasan sada zumunta har guda biyu, duk da cewa muna jiran gwamnatin tarayya ta bayyana ranar da za’a dawo a ci gaba da wasanni a fadin kasar nan”.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!