Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tallafa wa mabukata na kawo rahamar Ubangiji:   Dr Bashir Aliyu Umar

Published

on

Babban limamin masallacin Alfurkan dake Alu Avenue a karamar hukumar Nasarawa, Dakta Bashir Aliyu Umar, ya ja hankalin mawadata da su rika tallafawa raunana a cikin al’umma musamman ma a wannan lokaci da ake fama da matsin rayuwa sanadiyyar annobar Covid 19.

Dakta Aliyu Umar, ya bayyana hakan ne yayin rabon tallafin kudi da kayan situru da gidauniya tallafawa mabukata watau Ramadan Trust Initiative ta gudanar a masallacin na Alfurkan.

Limamin ya ce nuna jinkai ga juna a cikin al’umma na daga cikin abunda ke kawo saukar jinkan Allah ga al’umma.

A nasa bangaren mataimakin sakataren kungiyar Malam Umar Muhammad, cewa ya yi, sun raba tallafin ne ga mata domin su ja jari domin su dogara da kansu.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya rawaito cewa fiye da mabukata 50 ne suka amfana da tallafin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!