Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Wadanda suka kamu da Corona sun kai 936 a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da samun karin mutane 13 dauke da cutar Covid-19 a jihar a ranar Laraba.

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ce ta sanar da hakan a shafinta na Twitter a daren Larabar da misalin karfe 11:45 na dare.

Ma’aikatar lafiyan ta Kano ta ce an sallami karin mutum guda wanda ya warke daga cutar a ranar Laraban, sannan karin mutum 3 cikin masu dauke da cutar sun rigamu gidan gaskiya.

Yazuwa yanzu adadin masu dauke da cutar a Kano sun kai 936.

Mutane 135 daga ciki an sallame su bayan da suka warke sarai daga cutar.
41 daga ciki kuma sun rigamu gidan gaskiya.

Yanzu haka dai masu fama da Corona 760 ne ke cigaba da samun kulawar jami’an lafiya a cibiyoyin killace masu dauke da cutar dake Kano.

A ranar Alhamis dinnan ne gwamnatin Kano tace zata shiga zagaye na biyu na rabon tallafin rage radadin dokar zama gida kan Corona ga mabukata.

Wakiliyar Freedom Radio a fadar gwamnatin Kano Zahra’u Nasir ta rawaito mana cewa a ranar Alhamis din ne ake sa ran gwamna Ganduje zai bude cibiyar daukar samfurin gwajin masu cutar Corona a unguwar Sabon Gari dake Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!