Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Taron tattalin arziƙi: Mun daina dogara da man fetur – Buhari

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ce Najeriya ta mayar da hankali kan rage dogaro da arziƙin man fetir.

Shugaban ya ce, ya zuwa yanzu Najeriya ta mayar da hankali kan inganta harkokin noma da fasahar sadarwa da kuma ma’adinai.

Sannan ya ce, ta mayar da hankali kan yaƙi da cin hanci da rashawa da matsalolin tsaro da sauyin yanayi da ƙaddamar da shirin tallafawa al’umma.

Buhari ya bayyana hakan yayin taron saka hannun jari da ake gudanarwa a ƙasar Saudiyya karo na 5.

Taron wanda dama ce ta gabatar da buƙatu da suka shafi harkokin tattalin arziki, wanda za a shafe tsawon kwanaki 4 ana gabatar da shi a birnin Riyadh.

Kazalika taron ya ƙunshi shugabannin ƙasashe da manyan ƴan kasuwa masu saka hannun jari da bankuna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!