Connect with us

Labarai

Tashin farashin tikitin jirgi a Disamba ba shi da alaka da haraji- NCAA

Published

on

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta kasa NCAA ta bayyana cewa tashin farashin tikitin jirgin sama da aka samu a watan Disamba, ba shi da alaka da wani sabon haraji ko karin kudin gwamnati.

 

NCAA ta ce hauhawar farashin ya samo asali ne daga karuwar bukatar tafiye-tafiye a lokacin bukukuwan karshen shekara, tare da kalubalen kudin aiki da kamfanonin jiragen sama ke fuskanta, ciki har da tsadar man jirgi, kula da jirage da sauyin farashin musayar kudi.

 

Hukumar ta kuma ce ba ta amince da kara haraji ko wasu kudade a wannan lokaci ba, inda ta ce tana ci gaba da sa ido domin tabbatar da adalci a farashin tikitin jirgin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!