Connect with us

Labarai

Tinubu ya gana da shugaban rundunar sojin AFRICOM

Published

on

Shugaban Kasa  Bola Ahmed Tinubu, ya karɓi baƙuncin shugaban rundunar sojin Amurka ta Afirka AFRICOM, Janar Dagvin Anderson, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da ake ƙara tattaunawa kan haɗin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka, musamman wajen yaƙi da ta’addanci da sauran barazanar tsaro a yankin.

Yayin taron, Janar Anderson ya zo ne tare da tawagar AFRICOM da ta haɗa da Muƙaddashin Jakadan Amurka a kasar nan , Keith Heffern, Babban Mai Ba da Shawara kan Harkokin Waje na AFRICOM, Ambasada Peter Vrooman.

Shugaba Tinubu ya karɓi tawagar tare da manyan jami’an gwamnatin sa da suka haɗa da Mai Ba da Shawara kan Tsaro na Ƙasa, Nuhu Ribadu, Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa mai ritaya, Babban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede, Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!