Connect with us

Labarai

Tinubu ya gana da shuwagabannin NLC a Abuja

Published

on

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu, ya gana da shugabannin Kungiyar Kwadago ta kasa NLC a Fadar mulki ta Aso Villa da ke birnin tarayya Abuja a daren Talatar makon nan, a wani yunkuri na dakatar da shirin zanga-zanga a fadin kasar nan da ƙungiyar ta shirya yi kan matsalar rashin tsaro.

 

Rahotonni sun bayyana cewa, NLC ta sanar da shirya zanga-zangar ƙasa baki ɗaya a yau 17 ga Disamba, inda ta danganta hakan da abin da ta kira taɓarɓarewar halin tsaro a ƙasar nan.

 

Shugaban NLC, Joe Ajaero, ne ya jagoranci shugabannin ƙungiyar zuwa taron.

 

Bayan kammala taron, Ajaero bai bayyana matsayarsu ba kan zanga-zangar, inda NLC din ta ce, za ta sanar da matsayarta kafin gobe Alhamis.

 

Sai dai tun da safiyar yau Laraba ne aka gudanar da zanga-zangar a jihohin kasar nan.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!