Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Tottenham ta sallami mai horar da ita  Nuno Santo Espirito

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Tottenham da ke kasar Ingila ta sanar da sallamar mai horar da tawagar Nuno Espirito Santo, bayan watanni hudu daya kwashe yana jagorantar kungiyar.

Tottenham dai a karshen mako ta yi rashin nasara da ci 3-0 a hannun Manchester United a gasar Firimiya.

Kungiyar Spurs ta yi rashin nasara a wasanni 5 cikin 7 da ta buga.

Inda ta ke da maki 8 da tazarar maki 10 tsakaninta da mai jagorantar teburin gasar Chelsea.

“Mun dauki matakin sallamar   Nuno ne sakamakon yadda kungiyar ta mu a yanzu ta gaza samun nasararori, amma dai munsan irin gudunmawar da ya bayar a cigaban kungiyar a cewar daraktan wasannin na kungiyar Fabio Paratici.

Mai shekaru 47 dan kasar Portugal tin da fari ya amince da kwantaragin shekaru biyu a kungiyar

bayan shafe shekaru hudu ya na jagorantar Wolves.

Kungiyar kwallon kafa ta Totttenham dai ta ayyana cewa sallamar mai horar da kungiyar shine matakin da zai kawo mata nasarori a anan gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!