Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tsaro: Bayan shekara biyu an cafke wanda suka yi garkuwa da bature a Kano

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta cafke waɗanda ake zargi da kashe ɗan sanda tare da sace wani bature.

A ranar 16 ga watan Afrilu na shekarar 2018 ne wasu ‘yan bindiga suka buɗe wuta a titin Madobi inda suka harbe wani ɗan sanda Rabilu Musa.

Ƴan bindigar sun kuma ta fi da bindigar ɗan sandan tare da harsashi guda goma sha biyar.

Sannan suka yi awon gaba da wani Injiniya ɗan ƙasar Jamus mai suna Michel Cremza.

A ranar Talata jami’in hulɗa da jama’a na ƴan sandan Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanar da Freedom Radio kama waɗanda ake zargin bayan shafe shekara biyu.

Kiyawa ya ce, sun fara cafke wani matashi mai suna Abubakar Isma’il mai shekara 30 a duniya ɗan ƙauyen Wangara a ƙaramar hukumar Rimin Gado da ke Kano.

Binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin na da ruwa da tsaki wajen aikata ayyukan ta’addanci a Kano da Katsina da kuma jihar Kaduna a cewar Kiyawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!