Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Rahotonni

Zamu hukunta duk basaraken da ya fita daga Zamfara – Matawalle

Published

on

Gwamnatin jihar Zamfara ta haramta wa shuwagabannin al’umma fita daga yankunan su har tsawon wata uku.

Wadanda aka haramtawa fitar sun hadar da sarakunan jihar goma sha bakwai da shugabannin rikon kananan hukumomin jihar.

Gwamnan jihar, Muhammad Matawalle ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da Freedom Radio.

Gwamnan ya ce, an cimma wannan matsaya ne bayan tattaunawa da malaman addini da masu ruwa da tsaki kan sha’anin tsaro.

Labarai masu alaka

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta amince da sabuwar dokar ma’adanai

Na fara sayen Zinare don magance matsalar tsaro – Gwamnan Zamfara

A cewar sa, dama mutanen jihar sun dade suna basu makamanciyar wannan shawara, a don haka aka dauki wannan mataki.

Matawalle yace wannan abu ne mai kyau, kasancewar ko da wani abu zai faru to za a tuntubi gwamnati da jami’an tsaro cikin hanzari.

Haka kuma ya ce, ya basu wa’adin watanni uku don ganin an sami saukin al’amuran tsaro a jihar.

Gwamna Bello Matawalle a yayin da ya ke ganawa da ministar jin kai Hajiya Sadiya Umar Farouk kan matsalar tsaro.

Gwamnan ya kuma ce duk sarki ko shugaban karamar hukumar da aka sami matsalar ‘yan ta’adda a jihar sa, kuma baya nan to ya zama wajibi gwamnati ta hukunta shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!