Labarai
Tinubu ya gana da shugaban jam’iyyar SDP

Shugabannin jam’iyyar SDP da ƙungiyar IPAC sun jaddada bukatar a sake duba dokokin zaɓe domin tabbatar da sahihin zaɓe kafin babban zaɓen shekarar 2027. Sun bayyana hakan ne bayan wata ganawar sirri da suka yi da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja
.
Shugaban SDP na ƙasa, Farfesa Sadiq Umar Gombe, ya ce tattaunawar da suka yi da shugaban ƙasar ta mayar da hankali ne kan yadda za a ƙarfafa dokokin zaɓe domin dawo da amincewar jama’a ga tsarin dimokuraɗiyya. Ya ƙara da cewa ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen ƙananan hukumomin babban birnin tarayya Abuja, alama ce da ke nuna cewa mutane na rasa ƙwarin gwiwa ga tsarin zaɓe.
Shi ma shugaban IPAC na ƙasa, Dakta Yusuf Dantalle, ya bayyana cewa sun tattauna kan wasu batutuwa a dokar zaɓe, musamman tsarin zaɓen fidda gwani na kai tsaye ko na wakilai da kuma tura sakamakon zaɓe ta hanyar fasahar zamani. A nasa bangaren, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na SDP a zaɓen 2023, Adewole Adebayo, ya bukaci ‘yan siyasa da su guji mayar da zaɓen 2027 na “mutuwa ko rai”, yana mai cewa abin da ya fi muhimmanci shi ne nasarar Najeriya baki ɗaya.
You must be logged in to post a comment Login