Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

U-20 AFCON: Ghana ta bai wa kowa ne dan wasa kyautar dala dubu 10

Published

on

Shugaban kasar Ghana Nana Addo, ya ce, zai baiwa kowane dan wasan kungiyar kwallon kafa ta kasar ‘yan kasa da shekara 20 kyautar dala dubu 10 sakamakon nasarar lashe kofin Afirka.

Nana Addo ya yi wannan alkawarin ne a ranar Talata 9 ga watan Maris a wata ziyara da ‘yan wasan suka kai masa bayan dawowarsu daga kasar Mauritania inda suka buga wasan.

Shugaban ya kuma ce za a raba kudin kashi biyu inda kowa zai karbi kashi guda yayin da kuma za a saka hannun jari na tsawon shekaru 10 da kashi dayan.

Ghana dai ta lashe kofin ne bayan da ta doke Uganda da ci biyu da nema a wasan karshe na gasar cin kofin na Afirka na ‘yan kasa da shekara 20.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!