Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

UNICEF:Kimanin dalibai miliyan 8 ne basa zuwa makaranta a jihohin Najeriya 10

Published

on

Asusun kula da kananan yara na majalisar dinkin duniya yace jihohi 10 ciki har da babban birnin tarayya Abuja na da kananan yara miliyan 8 da basa zuwa makaranta.

Jihohin sun hadar da Bauchi da Niger, Katsina da Kano, Sokoto Zamfara Kebbi Gombe Adamawa da kuma jihar Taraba.

A wata sanarwa da asusun ya fitar a jiya Lahadi a yayin bikin ranar yaran nahiyar Africa wakilin asusun a nan Najeriya Peter Hawkings ya ce akwai bukatar a samar da ingantatccen ilimi ga kananan yara musamman mata.

Taken bikin kananan yara na nahiyar Afrika na bana shine yara na da damar samun ingataccen ilimi ko da kuwa a lokacin yaki ne.

Mr. Hawkings ya ce kimanin kananan yara miliyan 10 da rabi ne basa samun damar zuwa makaranta sakamakon ayyukan ta’addanci a yankun jihohin arewa maso gabashin kasar nan.

Ya ce rashin zaman lafiya ya yi sanadiyyar rufe makarantu, haka kuma ya hana malaman zuwa makaranta tare da sanya tsoro a zukatan iyaye wajen tura yaransu zuwa makaranta musamman yaran su mata wadanda sune suke cikin daliban da ‘yan ta’adda ke sacewa a makarantun su.

Mr.Hawkings ya ce akwai bukatar mahukunta a wadanan jihohi su daukin matakin gaggawa kan magance matsalar rashin zaman lafiya don tabbatar da cewa kananan yara sun samu ingantaccen ilimi tun daga matakin farko.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!