Connect with us

Labarai

Wajibi Nyesom Wike ya nemi afuwar shugaba Tinubu bisa cin mutumcin jami’in sojan Najeriya da ake zargin sa: Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai mai ritaya

Published

on

Tsohon Babban Hafsan Sojin Najeriya, Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai mai ritaya, ya bayyana cewa wajibi ne Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya nemi afuwa daga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma rundunar sojin Najeriya bisa abin da ya aikata wa wani jami’in soja.

 

Buratai ya ce abin da ya faru tsakanin Wike da sojojin ya nuna rashin girmama rundunar tsaro da kuma rashin bin tsarin doka, yana mai jaddada cewa bai dace jami’in gwamnati ya nuna wa jami’in soja irin wannan dabi’ar ba, musamman a bainar jama’a.

 

Ya ce Wike ya kamata ya bai wa Shugaban kasa, wanda shi ne Kwamandan Rundunonin Tsaro, da kuma sojojin kasar nan, hakuri bisa wannan lamari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!