Addini
Wani maniyyacin Najeriya ya rasu a kasar Saudiyya

Wani maniyyacin daga cikin alhazan jihar Abiya ya rasu a birnin Makka.
Marigayin mai suna Alhaji Sale, wanda shi ne shugaban kasuwar shanu ta Lokpanta da ke jihar Abiya, ya rasu ne a daren jiya Litinin.
Wakilin hukumar aikin hajji ta Najeriya NAHCON, Alhaji Ibrahim Orjibulam, ne ya tabbatar da rasuwar mamacin.
Sanarwa ta ce, ana sa ran yi wa marigayi Alhaji Sale, jana’iza yau Talata a masallacin Harami da ke Birnin Makka.
Rahotonni sun bayyana cewa, wannan ne karo na biyu da aka samu rasuwar alhazan Najeriya bayan rasuwar wata mata ‘yar asalin jihar Edo.
You must be logged in to post a comment Login