Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Wani matashi yayi garkuwa da wani yaro a Kano

Published

on

Anyi nasarar damke matashin ne a lokacin da ake zargin shi da yin garkuwa da wani yaro dan shekaru goma, bayan da iyayen yaron suka yi kararshi.

Matashin wanda dan uwan matar ne ya nemi masauki a gidan, inda matashin yayi amfani da wannan dama ta hanyar yin garkuwa da dansu mai shekara goma.

Matashin ya bukaci Naira dubu dari uku a matsayin kudin fansa, bayan iyayen yaron sun biya wannan kudi sai ya kasha shi ya kuma jefar da gawarsa a kauyen Minjibir.

Rundunar ‘yan sanda ta Kano ta yi holin masu yin garkuwa da mutane

Masu dauke da cuta mai karya garkuwa na fuskantar tsangwama- Nuhu Tela

Masu garkuwa da mutane sun sace dan jaridar Borno

Iyayen yaron sun bayyana cewa  sun ji labarin an tsinci gawar dansu a kauyen Minjibir, inda suka tarar har mutanen da suka tsinci gawar yaron sun yi jana’izar sa kamar yadda addinin Islama ya tanada.

‘jami’an ‘yan sanda dai sunyi nasarar kamo wannan matashi a jihar Kaduna, tare da gurfnar dashi a gaban  kotu domin girbar abin da ya shuka.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!