Connect with us

Labaran Wasanni

Wasanin kafafan yaɗa labarai: Freedom Radio ta fito a rukunin C

Published

on

Hukumar wasanni ta jihar Kano ta ce, za ta ci gaba da bada goyon baya ga ƙungiyar marubuta labarin wasanni ta kasa reshan Jihar Kano SWAN.

Shugaban hukumar Alhaji Ibrahim Galadima ne ya bayyana haka a yayin taron fitar da jadawalin wasan gasar ƙwallon ƙafae kafafan yaɗa labarai na Jihar kano.

Alhaji Ibrahim Galadima
Galadima ya ce lokaci ya yi da kamfanoni za su sanya hannun jarinsu a ɓangaren wasanni.

A nasa jawabin shugaban kamfanin da zai ɗauki nauyin shirya gasar Dala Inland Dry port Alhaji Ahmad Rabiu ya ce sun shiga gasar ne da nufin bunƙasa harkokin wasannin.

Har ma ya yi kira ga sauran kamfanoni da su shigo harkokin wasanni don ganin an ƙara bunƙasa jihar kano.

A yayin fitar da jadawalin wasannin Freedom Radio ta fito a rukunin C.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!