Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ma’aikatan KEDCO sun rasu sanadiyyar hatsari

Published

on

Wasu ma’aikatan kamfanin rarraba wutar lantarki shiyyar Kano KEDCO guda biyu sun rasa rayukan su, sanadiyyar hatsarin mota da ya rutsa da su a kan hanyar su ta dawowa Kano daga jihar Katsina.

Hakan na cikin wata sanarwar da jami’in hulda da jama’a na kamfanin Ibrahim Sani Shawai ya fitar.

Sanarwar ta ce, wadanda suka rasun sun hada da Malam Nazir Ahmad da Malam Abdurra’uf Ahmad.

Sanarwar ta kara da cewa, hatsarin ya faru ne sakamakon fashewar tayar motar a karamar hukumar Kankiya wanda yayi sanadiyyar hatsarin, tare da jikkata mutane shida.

Yayin da direban motar da wani guda mai suna Mr Johnson suka tsira ba tare da samun  ranuni ba.

Kazalika, sanarwar ta bayyana cewa tuni aka dauko gawarwakin wadanda suka rasu zuwanan  Kano don yi musu jana’iza sauran kuma aka kai su asibiti don ci gaba da duba lafiyar su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!