Labaran Kano
Wasu ‘yan ta’adda sun kai mummunan hari a jihar Katsina

Rahotanni daga Jihar Katsina na nuni da cewa ‘yan bindiga sun kai hari a ƙauyen Doma, da ke Tafoki Ward a Ƙaramar Hukumar Faskari, inda suka kashe mutane da dama.
An ce harin ya faru ne da rana tsaka, inda maharan suka shafe sa’o’i suna barin wuta kafin su janye da misalin ƙarfe huɗu na yamma. Yayin da harin ya yi sanadiyyar konewar wasu gidaje a yankin
Shugaban yankin, Alhaji Surajo Aliyu-Daudawa, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai bayyana harin a matsayin ramuwar gayya, kuma mafi muni cikin watanni biyar da suka gabata, duk da yarjejeniyar zaman lafiya da aka taɓa cimmawa da ‘yan bindigar.
Sai dai rundunar ‘yan sanda ta ce mutane 13 ne suka mutu, inda ta bayyana cewa jami’anta tare da sojoji sun kai ɗauki, amma maharan sun tsere kafin isowarsu.
You must be logged in to post a comment Login