Coronavirus
WHO : Za mu yi bincike kan rigakafin Corona da Rasha ta samar
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/08/WHO-1.jpg)
Hukumar lafiya ta Duniya WHO ta ce sai ta yi kwakkwaran nazari kan ingancin allurar cutar corona da kasar Rasha ta yi ikirarin samarwa kafin sahale masa.
A yau talata ne dai kasar ta Rasha ta sanar da cewa ta kirkiro da allurar cutar ta covid-19.
Mai magana da yawun hukumar ta WHO Tarik Jasarevic, ya sahidawa manema labarai yau a birnin Geneva da ke kasar Switzerland da cewa, tuni suka tuntubi hukumomin kasar ta Rasha don tabbatar da ingancin allurar rigakafin.
Ya ce duk wani magani da za a samar a duniya wajibi ne hukumar ta tabbatar da inagncinsa kafin fara amfani da shi.
Tun farko dai kasar ta Rasha ta yi ikirarin cewa an kirkiro da allurar cutar ta covid-19 ne a cibiyar bincike ta Gamaleya
You must be logged in to post a comment Login