Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

WHO : Za mu yi bincike kan rigakafin Corona da Rasha ta samar

Published

on

 

Hukumar lafiya ta Duniya WHO ta ce sai ta yi kwakkwaran nazari kan ingancin allurar cutar corona da kasar Rasha ta yi ikirarin samarwa kafin sahale masa.

A yau talata ne dai kasar ta Rasha ta sanar da cewa ta kirkiro da allurar cutar ta covid-19.

Mai magana da yawun hukumar ta WHO Tarik Jasarevic, ya sahidawa manema labarai yau a birnin Geneva da ke kasar Switzerland da cewa, tuni suka tuntubi hukumomin kasar ta Rasha don tabbatar da ingancin allurar rigakafin.

Ya ce duk wani magani da za a samar a duniya wajibi ne hukumar ta tabbatar da inagncinsa kafin fara amfani da shi.

Tun farko dai kasar ta Rasha ta yi ikirarin cewa an kirkiro da allurar cutar ta covid-19 ne a cibiyar bincike ta Gamaleya

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!