Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ya kamata a baiwa mahajjata damar ciyar da kansu-Gagaci

Published

on

Dagacin Garin Dan Hassan dake yankin karamar hukumar Kura a nan Kano Alhaji Adda’u Sani ya shawarci hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON data baiwa Alhazan bana dama kowa ya ciyarda kansa a lokacin gudanarda ibadar aikin Hajjin bana sakamakon matsalar da ake yawan samu ta abinci a kasa mai tsarki.

Alhaji Adda’u Sani ya bayyana hakan ne a yayin zantawarsa da manema labarai.

A cewarsa “Alhazai suna biyan kudin abinci mai yawa, amma sai ka iske ana baiwa Alhazan abincin da bashi suke bukata ba, amma idan aka baiwa kowa dama ya ciyarda kansa za’a magance duk wata matsalar abinci a tsakanin Alhazan Najeriya”.

Freedom Radio ta ruwaito Dagacin Garin na Dan Hassan Alhaji Adda’u Sani ya koka kan yadda a bana aka samu matsalar tashin farashin kudin kujerar aikin Hajjin bana da hakan ke nuna cewa duk Alhajin da yake bukatar zuwa aikin Hajji a wannan shekarar wajibi ne ya biya naira miliyan hudu da dubu dari biyar a matsayin kudin farko.

 

Rahoton: Abdulkarim Muhammad Abdulkarim

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!