Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

CP Singham ya musanta zargin ya rasu

Published

on

Tsohon kwamishinan ‘yan sanda  na jihar Kano Muhammad Wakili ya musanta  zargin da ake yadawa  cewa ya rasu.

CP Muhammad Wakili mai ritaya ya bayyana hakan ne a tattaunawar sa da wakilin mu Hassan Muhammad Auwal a gidan sa dake jihar Gombe.

Tsohon kwamishinan yada labarai ya ce labarin bai bashi mamaki ba kasancewar  masoya sun ta tuntubar sa.

Tun a jiya ne wasu kafafan sada zumunta  suke yadawa cewa,  tsohon kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano, Muhammad Wakili  ya rasu.

An ta yi ta yada jita-jitan cewa Tsohon kwamishinan ‘yan sandan wanda aka fi sani da Singham ya rasu a wani mumunan hadarin mota da ya afko.

Akan haka ne mutane  suka yi ta bayyana alhinin su da jimami kan rasuwar ta sa a kafafan sada zumunta.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!