Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

COVID-19 : UNICEF na ziyartar makarantu a Kano

Published

on

Asusun tallafawa kananan yara na majalisar dinkin duniya wato Unicef ya fara ziyartar makarantun Firamare dake fadin jihar Kano domin duba kayayyakin kariya na Covid 19 da suka rabawa makarantun Firamare.

Sakataren Ilimi na asusun tallafawa kananan yara dake aiki a Najeriya  Nasaka Adebayo Ibrahim ya bayyana hakan yin da suka kai ziyara karamar hukumar Kunchi.

Nasaka Adebayo Ibrahim ya ce sun fara kai ziyarar ne domin tabbatar da makarantun furamare suna kiyaye dokar Corona musamman ma a yankin karkakar

Yace sun raba abubuwan wanke hannu a makarantun Firamari bisa duba adadin yawansu domin tabbatar da an dakile yaduwar cutar Corona a tsakanin dalibai.

Malam Mati Sha’aibu guda ne daga cikin malaman makaranta ana Kano yace iyayen yara basa son turo yara su makaranta sai dai su turasu kasuwa.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa dukkanin makarantun suna bukatar malamai da kayayyakin koyo da koyarwa .

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!