Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yadda guda daga cikin manyan kwamandojin kungiyar boko Haram ya mika wuya

Published

on

Shalkwatar tsaron kasar nan tace wani guda daga cikin manyan kwamandojin kungiyar boko Haram ya mika kansa ga shalkwatar tasu tare da matansa guda hudu bayan wata karan batta da sukayi da jami’an sojin a tsakanin sha bakwai ga watan da muke ciki zuwa Ashirin da uku ga watan na Satumba.

Mai Magana da yawun rundunar Manjo Janar John Enenche ne ya bayyana hakan a wani taron karshen mako-mako da rundunar take gudanarwa a birnin tarayya Abuja.

Manjo John Enanche ya kuma ce nasarar da suka samu ta biyo bayan wata musayar wuta da aka yi tsakanin dakarun Operation Lafiya Dole da ‘yan tada kayar bayan a Jihohin Borno da Taraba da kuma Adamawa.

Ya kuma ce a Borno sun yi nasarar kama mutum guda a karamar hukumar Kamuya a karamar hukumar Biu a jihar Borno yayin da sauran mutane Tara aka kama su ne a karamar hukumar Wukari dake jihar Taraba.

Manjo Janar John Enanche ya kuma ce a yayin musayar wutar rundunar tayi nasarar kwato wasu motoci da sauran kayayyakin da suke ta’addanci da su

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!