Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yajin aiki: Dalilan da suka sanya NLC ta yi watsi da umarnin kotu

Published

on

Ƙungiyar kwadago ta Jihar Kano ta umarci mambobinta su tsunduma yajin aikin sai baba ta gani daga ranar litinin mai zuwa har sai sunji sanarwa daga ƙungiyar.

Shugaban ƙungiyar ta Kasa reshen Jihar Kano Kabiru Ado Mijibir ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan kammala tattaunawa da shugabanin ƙungiyoyin ƙwadagon a nan Kano.

Mijibir, ya ce, tafiya yajin aikin ya zama dole saboda yanayin da aka tsinci kai na tsadar rayuwa da kuma ƙarin farashin man fetur wanda hakan ya ƙara jefa rayuwar ma’aikata da masu ƙaramin karfi cikin mawuyacin hali.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad, ya ruwaito shugaban ƙungiyar na kira ga sauran ƙungiyoyin da ɗaiɗaikun jama’a su bai wa ƙungiyar ƙwadagon hadin kai don samarwa jama’a mafita daga yanayin tsadar rayuwa da ake ciki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!