Connect with us

Labarai

Yadda rundunar soja ta kasa ta kashe gawurtaccen dan fashi

Published

on

Rundunar sojin kasar nan ta ce ta kashe gawurtaccen dan fashin nan mai suna Terwaza Akwaza da ya addabi al’ummar jihar Benue.

A jiya talata ne sojoji a jihar ta Borno suka sanar da Mutuwar Terwaza Akwaza wanda aka fi sani da Gana .

Ta cikin wata sanarwa da Babban Kwamanda mai kula da rundunar soji ta musamman ta hudu, Birgediya Maude Ali Gadzama ne ya fitar ga manema labarai.

Birgediya Maude Ali ya ce sojojin sun sami nasarar Bude wuta ga tawagar tantiran da adadinsu ya kai 172 ciki har da Gana.

Sai dai a yayin arangamar sojojin sun sami nasarar Kwace bindigogi kirar Ak 47 da kuma kananan bindigogi da kuma tarin alburusai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!