Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

‘Yan bindiga sun kashe shugaban Fulanin yankin Doka a Kaduna – Aruwan

Published

on

Wasu da ake zargin ‘Yan bindiga ne sun kashe wani shugaban Fulani a yankin Doka da ke karamar hukumar Kajuru, a jihar kaduna Alhaji Lawal Musa, wanda aka fi sani da Alhaji Maijama’a.

Kwamishinan Tsaro da harkokin cikin gida na jihar Samuel Aruwan ne ya tabbatar da faruwar lamarin a daren jiya Litinin 22 ga watan Mairs.

Ya ce wasu ‘yan fashi sun kashe Alhaji Lawal Musa a gaban danginsa a ranar Lahadin da ta gabata.

Kwamishinan ya ce, Alhaji Lawal Musa ya kasance shugaban al’ummar Fulani a cikin babban yankin nasu kuma ya yi aiki kafada da kafada da sauran shugabannin al’ummar wajen kokarin samar da zaman lafiya.

A cewer sa marigayin na zaune da dan uwansa Alhaji Gide Musa, kwatsam sai maharan suka bullo tare da bude musu wuta, lamarin da yayi sanadiyyar tserewar Alhaji Gide Musa wanda hakan ya basu damar yi masa yankan rago.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!