Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

‘yan bindiga sun sace tare da yin garkuwa da wasu fasinjoji a garin Fatakwal

Published

on

‘Yan bindiga sun sace tare da yin garkuwa da fasinjojin wata mota da ta tashi daga garin Abua zuwa garin Fatakwal a jihar Rivers.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a jiya laraba a daidai mahadar hanya ta Rumuekpe da ke yankin karamar hukumar Emohua a jihar ta Rivers.

Wani shaidan gani da ido ya shaidawa manema labarai cewa, ‘yan bindigar sun yi kofar rago ne ga motar bayan sun fito daga cikin daji,  sannan su ka fara harba bindiga sama.

Ya kuma ce bayan sun tsorata mutanen da ke daf da wajen da lamarin ya faru ne, sai suka tasa keyar fasinjojin goma tare da direban su zuwa cikin daji da ke kusa da wajen da lamarin ya faru.

Sai dai anata bangaren rundunar ‘yan sanda a jihar Rivers ta bakin mai magana da yawunta, Nnamdi Omoni, ta ce har ya zuwa yanzu ba ta samu labarin faruwar lamarin ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!