Connect with us

Labarai

Yan bindiga sun yi wa jami’an tsaro kwanton bauna a Kebbi

Published

on

Akalla sojoji 11 da jami’in ‘yan sanda guda 1 ne rahotanni suka ce wasu ‘yan bindiga sun yi musu kwanton bauna a kauyen Giro Masa da ke karamar hukumar Shanga a jihar Kebbi.

 

Harin dai ya faru ne a daren ranar Talata inda jami’an tsaro da ake kyautata zaton sun dade suna gudanar da ayyukansu a yankin, suka gano ‘yan bindigar a farfajiyar wani kamfanin gine-gine.

 

Bayan da aka samu labarin an tura sojoji domin su tsare wurin amma yan bindigar sunyi musu kwanton bauna a hanya, inda Jami’in dan sanda da sojoji sun rasa rayukansu a harin tare da kona motocin sojoji biyu.

 

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya ziyarci wadanda suka jikkata a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Birnin Kebbi. Bayan ziyarar, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da rashin tausayi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!